1 Nuwamba 2024 - 18:23
Jaridar Yahudawa: Isra’ila Tasha Kayi Awajen Hizbullah / Runduna 7 Da Biyu Na Kota Kwana Sun Gaza Hatta Mamaye Kauye Daya Na Lebnon

Yadda jaridar yahudawan sahyoniya tayi suka kan sojoji Isra’ila da cewa: Rundunar kasa 7 ba su ma iya mamaye ko da kauye daya ba na lebnon.

Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul Bait (As) - ABNA - ya habarta cewa: wannan Jaridar Ibrananci Yediot Aharonot ta kawo shafinta cewa: manyan rundunonin Isra’ila biyar da wasu rukunin rundunoni biyu na kota kwana ba su iya mamaye ƙauye ɗaya a kudancin Lebanon cikin makonni huɗu ba.

A halin da ake ciki dai, wannan adadin dakarun soji ya ninka adadin wadanda suka halarci yakin kwanaki 33 har sau 3.